A ranar Asabar ce aka fara hidimar jana’izar tsohon jagoran addinin Iran, Ayatollah Ali Khamenei, wanda ya...
Latest News
Shugaban Kungiyar Fulani ta Miyetti Allah Kautal Hore, Alhaji Abdullahi Bello Bodejo ya karyata...
Hukumar Kula da Shaidar Ɗan Ƙasa (NIMC) ta ƙara ƙarfafa haɗin gwuiwa da manyan ma’aikatun gwamnati domin...
Wasu da ake zargin Boko Haram ne sun kai hari sansanin sojoji guda biyu...
Mata mabiya addinin Kirista da ƴan’uwansu Musulmai, sun ce mutunta ƴancin addinai ita ce hanya ɗaya tilo...
Aƙalla mutum biyu ne suka rasu, yayin da wasu suka jikkata sakamakon ruwan sama...
Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa, ta mayar wa gwamnatin jihar bashin Naira...
To, waɗansu malamai suka ce menene ma’anar “gayyu” wannan rufi? Suka ce ma’anarsa, idan mutum ya yi...
Farfesoshi tagwaye, Hassan Ishaƙ Ibrahim da Hussaini Yusuf Ibrahim tagwaye ne masu kama ɗaya tun daga ƙuruciya...
Shugaban kungiyar Fulani ta Miyetti Allah Kautal Hore, Alhaji Abdullahi Bello Bodejo ya karyata zargin da a ke yi masaa kan aikata laifuka 12 da ya hada da halatta kudin haramun da kuma hannu a tallafa wa ayyukan ta’addanci. Bodejo wanda ya gurfana a gaban babban kotun tarayya da ke Abuja a ranar Alhamis na maida bayani ne a kan zargin da a ka gabatar a kansa da Hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta EFCC ke yi, a karkashin mai sharia Inyang Ekwo. A yayin fara shari’an a karo na farko, Hukumar ta bakin lauyanta Wahab Shittu, ta zargi shugaban na Miyetti Allah da aikata laifin hallata kudin haram da ta ce ya kai dalar Amurka milayan 2 da doriya. Bayan karyata tuhumar da ke yi masan, lauyan Hukumar EFCC ya bukaci kotun da ta sa ranar fara sauraron bayanai a kan karar da su ka shigar, sai kuam bukatar cigaba da tsare shi har zuwa lokacin. Da ya ke mayar da martini, lauyan Shugaban na Miyetti Allah mai suna Ahmed Raji ya bukaci kotun da ta bada belin jagoran kamar yadda ya ce ya gabatar tun a farko. Lauyan ya shaidawa kotun cewa laifin da a ke tuhumar wanda ya ke karewan na cikin rukunin wadanda doka ta amince a bada beli a kansu, bukatar da lauyan EFCC ya bayyana ja a kai. A karshe kotun ta bada umarnin a cigaba da tsare wanda a ke tuhumar a hannun Hukumar ta EFCC, tare da sanar da ranar 20 ga watan nan ta Yuli a matsayin ranar yanke hukunci a kan bukatar bada belinsa.
